Wata sanarwa daga gwamnatin Nijar, ta ce sojojin ƙasar za su kai wa masu tsaron fadar Bazoum hari idan ba su janye ba. Wata majiya na cewa a halin yanzu ana kokarin tattaunawa domin sassanta lamarin. Hakan duk na faruwa ne bayan masu tsaron fadar sun tare hanyar gidan, lamarin da ya janyo fargaba a ƙasar.